Home Page
 Tarihin rayuwarsa
   Akidojin Shi'a
   Littafansa
   Fatawoyi
   Sakonni
   Darussa
   Littafan dansa
   Dakin karatu
   Hotuna


Affiliate Websites
Affiliate Websites

   E-Mail Listing:


 

Sakonnin Marja'in addini maigirma Ayatullahi Fadhil Lankarani dangane da shahadar Sayyida Zahra(a.s.)

1
Da sunan Allah mairahma maijinkai

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da amincin Allah sun tabbata ga manzon tsira Muhammad s.a.a.w. da iyalansa tsarkaka, musamman Siddikatu shahida Sayyida Fatimatu Zahra a.s. hushin Allah ya tabbata akan makiyansu baki daya.

 Wadannan kwanuka sun dace da lokacin zagayowar shahadar sayyida Zahra a.s. wadda take wata hakika ce wadda ta gagari masana da masu bincike su fahimci hakikanin samuwarta a.s.  An ambace da Fatima domin ta gagari halittu sanin hakikaninta. Itace wadda manzon Allah yake hushi da hushinta haka nan  Allah madaukaiki yake hushi da hushinta, sannan Allah da manzo suna farin ciki da farin cikinta. Sayyida Zahra a.s. bayan kasancewarta a matsayin cibiyar ma’abota kisa (mayafi) sanann itace matattarar Ahlulbait a.s. acikin ayar tathir (33:Ahzab). Nufin Allah ya ta’allaka akan ya tafiyar da dukkan kazanta daga ahlul bait ta hanyar  samuwarta. A matsayinmu na masu alfahri da kasantuwarmu mabiya wannan sayyida mai girma. Ya zama tilas akanmu a wannan zamani mu fahimci hakikanin koyarwar wannan sayyida mai girma da daukaka, domin  kada mu kasa aiwatar da nauyin day a hau kanmu. Saboda haka dole ne malamai a dukkan garuruwan musulmi da masu wa’azi su bada muhimmacin dangane da sanar da al’ummar musulmi hakikanin wannan baiwar Allah, bayan tarurruka da zaman makokin akan shahadar sayyida Zahra a.s su fadarkar da al’umma akan hakikanin koyarwa sayyida a.s. Alhamdu lillah mazhabar shi’a tare da amfani da dalilai da hujjoji da suka dace da hankali sun dauki nauyin wannan al’amari mai muhimamanci.

  A yau makiya sun fahimci cewa idan har musulmi suna bisa akidunsu na hakika, to ba zasu iya samun dammar iko akan al’amuransu ba, don haka suka yi aniyar gusar da akidun gaskiya na musulunci ta yadda wata rana musulmai zasu iya daukar makoki akan shahadar sayyidu shuhada a.s. da kuka akan shahadar Zahra wani abu ne marar amfani da manufa, ko su yi shakku akan zaluncin da aka yi wa Zahara a.s. duk da yake cewa wani abu ne wanda yake tabbace a bayyane acikin tarihin musulunci.

  Makiya su sani idan suna nufin su sanya shakkau da shubha akan shahadar Zahra a.s. to sam ba zasu iya kawar da zalunci da aka yi akan zahra a.s. ba  abayan wafatin manzo a.s. gajartar rayuwarta da hudubobin ta gabatar a massalacin manzo wadanda suke cike da hujjoji akan zalunci da aka yi mata, da kukan dare da rana da ta kasance acikinsa, da kariyar da ta dunga yi akan wilayar Imam Ali a.s. dukkan wannan dalilai ne akan zaluncin da aka aiwatar akanta a.s. Ta wanan fuskar duniyar musulmi da mijinta wanda ya ka sance acikin bakin ciki a koda yaushe.

   Juyin musulunci na Iran ya samo asali ne daga muhimmanci da al’ummar Iran suke bai wa wannan al’amari na shahadar Zahra a.s. da makamantansu. Saboda haka a yau daya daga cikin abubuwan da zasu kare wanann juyin musulunci shi ne bai wa irin wadanan abubuwa muhimmanci. Saboda haka wajibi ne kan mumimani su bai wa ranakun shahadar Sayyida Zahra a.s. muhimmanci, ka da su bari wannan waki’a mai muhimmanci ta  bace tsakanin abubuwan yau da kullum. Musammam ranar 3 Jumada thani ranar da jamhuriyar musulunci take yin hutu na kasa baki daya wanann yana nuna muhimmancin wannan al’amari ga jamhuriyar musulunci ta Iran. Muna fata Allah madaukaki ya yi mana muwafaka mu kasance acikin wadanda suke bai wa wannan al’amari muhimmanci ta yadda zamu samu ceton sayyida zahara a.s. da ‘ya’yanta tsarkaka.

 Tsira da amincin Allah su tabbata ga dukkan ‘yan’uwa muminai da rahmarsa.

Muhammad Fadhil Lankarani
30-5-80

2
Da sunan Allah mairahma maijinkai

Allah madaukakin sarki yana cewa:Lallai wadan da suke cutar da Allah da manzonsa tsinuwar Allah ta tabbata akansu acikin duniya da lahira, sannan ya yi musu tanadin azaba mai kuna” Ahzab. Sannan manzo yana cewa Fatima tsoka cedaga gareni duk wanda ya cutar da ita ya cutar da ni.

  Daya daga cikin muhimmin  alfahrin shi’a shi ne kasantuwar shugaban matan duniya da suke da ita wato sayyida Zahra a.s. wadda take da matsayin Isma. Bisa ga ayar Tathir wadda ta sauka akan mutane biyar wanda a samansu shi ne manzo s.a.a.w. Allah madaukaki ya tafiyar da kazanta daga gare su, sayyida Zahara tana daya daga cikin wadannan bayin Allah wadanda Allah madaukaki ya tsarkake su. Saboda haka fahimtar hakikanin zatin sayyida Zahra wani abu ne wanda yake da wahala ga sauran alumma.

 Sayyida Zahra Itace Farkon wadda ta samu rabon shahada daga cikin iyalan gidan manzo s.a.a.w. Sannan daga cikin alfahrin sayyida shi ne ita ce uwar sauran ahlul bait a.s.

  Sayyida Zahra a.s. ta kasance wata mata ce wadda ta kasance a cikin matukar zalunci da bakin ciki, musamman rashin mahaifinta manzo s.a.a.w. ammam acikin wannan halin ne wanda zai yi wa mutum wahala ya iya koda Magana ne amma sayyida Zahra a.a.s ta kasance ta aiwatar da huduba mai girgiza zukata a gaban masu iko na wanann zamani abin da ya gagari masana fahimtar matukar wannann al’amri, wato ta yaya ya ksance mace zata iya aiwatar da wannan huduba mai ratsa zukata a kuma cikin wannan yana yi da ta samu kanta. Hudubar sayyida Zahra a masallacin manzo ta kunshi abubuwa masu dama wadan  da suka hada tauhidi, annabta da imamanci, haka nan ta yi tsokaci da  Allah wadarai da abin da masu neman duniya suka aikata na kin gaskiya sannan suka rufe bakinsu akan ganin zalunci da aka yi wa wasunsu.

  Babu shakka dole ne mu yi ikirari bayan shekara dubu da dari hudu da cewa, ba mu iya sanin hakikanin wannan baiwar Allah ba, abin da kuma ya fi komi bakin ciki shi ne ta yadda wasu ta fuskar dalilai daban-daban suke neman su yi inkarin wannan zalunci da aka yi  wa‘yar ma’aiki Zahra a.s.

  Babu shakka wanann al’amari zai yi wuyar fahimta ga sauran mutane, ta yadda wata mata sakamakon kamalar da ta samu ya zamana yardarta yardar Allah madaukakin sarki ce.

  Lokutta da dama an rububuta abubuwa da dama wadanda basu da hakika akan sayyida Zahra a.s. bisa adawa  da kiyayya, wanda dukkan mai son gaskiya zai yi bakin cikin da hakan. Babu shakka al’amari hadin kai tsakanin al’ummar musulmi wani abu ne mai muhimmanci wanda shugaban juyin musulun Imam kohmain ya yi kira zuwa gare shi, amma wannan ba yana nufin cewa  shi’a su bar abinda suke da imani da shi ba, sannan su tsaya suna kallon irin karya da kage da ake yi akan sayyida Zahra a.s. babu shakka abin da Imam yake nufin shi  ne al’ummar musulmi su hada kansu wuri guda ta yadda zasu tunkari makiya musulunci baki daya, ta yadda makiya musulunci kada su samu damar cutar da muslunci.

  Saboda haka ya wajaba ga al’umar musulmi kwansu da kwarkwata ranar litinin wadda ta dace da uku ga Jumada Thani  bisa ingantacciyar ruwaya, wadda take nuni da cewa a wannan ran ace Sayyida Zahra a.s. ta yi shahada, saboda haka ne gwamnatin musulunci ta Iran ta bayar da hutu domin masu juyayi da wannan rana su fito domin nuna bakin cikinsu akan wannan zalunci da aka yi wa Zahra a.s. wanda  ya sanya ta yi shahada a wannan rana. Saboda haka musulmi ya kamata su bayar da muhimmmaci wajen gudanar da juyayi a wannan rana fiye da kowane lokaci. Babu shakka nuna ko-in-kula akan wannan al’amari yana tasirinsa marar kyau ga  dan Adam.

Tsarki ya tabbata ga dukkan bayi na kwarai.

Muhammad fadhil Lankarani
18-5-81.

3
Da sunan Allah mairahma maijinkai

Dangane da abin da na rubuta shekarar da ta gabata game da abin da ya shafi shahadar Sayyida Zahra a.s. to wnanan cigaba ne akan hakan. Girmama wanann rana ta shahadar Zahara wadda ita ce ta farkon acikin shahidan iyalan gidan manzo s.a.a.w. yin hakan yana matsayain jaddada wilayarmu zuwa ga iyalan gidan manzon tsira s. da nuna godiyar bisa cikar ni’mar da Allah madaukaki ya yi mana na cika addininsa.

 Fatima Zahra wadda yardarta yrdar manzo kuma yardar Allah s.w.t ce,kuma fushinta fushin Allah da manzo ne.

  Fatima zahara a.s  wadda A’imma dinmu suke alfahri da kasantuwar mahaifiya ce a gare su, wadanda su ne cikakkun mutane kuma halifofin Allah a bayan kasa. Fatima a.s. duk da cewa ba ta rayu ba tsawon lokaci amma ta yiwa shi’anci hidima ta har abada, Sayyida Zahra a.s. ta tsoratar da makiya ta hanyar hudubarta mai raza zukata.

 Zahra a.s. ta isar da bakin cikinta na rashin mahaifinta  da zalunci da aka yi wa mijinta, ta hanyar kuka acikin gari da wajen madina wanda har yanzu akwai tasirin muryar kukanta a garin madina.

  Mu ‘yan shia muna alfahri da cewa mun koyi hakikanin addini daga ‘ya ‘yan sayyida Zahra a.s. ilimin da ya dace da hankali kuma ya dace da kowane zamani da kowane wuri. Sanann yana kunshe da dukkan bukatocin bil adama. Ta hanyar koyarwar ‘ya’yan Fatima ne al’ummar Iran suka samu damar tsayuka da fito na fito akan azzalumai, ta yadda suka iya samun ‘yanci da izza.

  Ta wannan fuskar ne makiya musulunci suka dauki alkawarin cewa lallai sai sun raba mutane da Ashura, sha’aban da ramadhan ta haka ne zasu iya cimma mummunan nufinsu.

  Anan tunatar da wannan batu wani abu ne wanda ya wajaba, rayar da wadannan ranaku da yin juyayi akan wadannan ranaku yana da ga cikin ayyukan Imam khomain wanda babu wani wanda yake shakku akan haka. Sanann yin hakan ba ya da akala da batun hadin kan al’ummar musulmi. Wanann hadin kai wani abu wanda Ayatullahi Burujardi shima yake matukar ba shi muhimmanci, amma wannan ba yana nufin cewa shi’a su manta da akidunsu ba, abin nufi anan shi ne hadinkan musulmi ta yadda zasu fuskanci makiya addinin musulunci, wadanda bisa jagoranci sahaniya suke neman suga bayan musulmi da muslunci baki daya.

 Saboda haka ya zama wajibi akan akan al’ummar musulmi a ranar uku ga wata wanda jamhuriyar musulunci take bayar da hutu don gudanar da juyayin shahadar Zahra a.s. su gabatar da zaman makoki dangane da wannan rana. Ta yadda zasu yi gungu a bisa tituna suna nuna bakin cikinsu da wannan rana.

 “Suna so su gusar da hasken Allah, amma Allah ya ki  domin yana son cika haskensa koda kafirai sun ki”.

Muhammad Fadhil Lankarani
7-5-1382

4
Dasunan Allah mairahma maijinkai.

Mun samu kanmu acikin kwanukan shahadar Fatima a.s. wadda ta kasance mahaifiyar  babanta wato manzo kuma mahaifiyar A’imma a.s. wadda ta kasance cibiya ce ga iyalan gidan manzo, kuma wata alama ce ta sirrin halittar Allah madaukai, wadda hatta  ‘yan shi sun gagara su san hakikanin samuwarta. Wadda take hakika ce ta haske wadda ta hanyar adawa da zalunci ta buya ga muatane har ya zuwa ranar kiyama.

  ‘yan shia kai da dukkan halittu da mala’iku suna alfahri da samuwar Zahra a.s. Alkauthar wadda ta zama sanadin wanzuwar addinin manzo s.a.a.w. wanda ta haka ne duniya ta cika da koyarwar ‘yan ‘yanta tsarkaka. Shin da Zahra ba ta ksance ba, wane irin duhu duniya zata kasance acikinsa.. bias umurninin ayar nan da take cewa “ka ce ban tambaye ku lada ba sai son makusantana” ta wajabta wa dukkan al’umma soyayya ga iyalan gida manzo wato ahlul bait a.s. wadda a samansu it ace Fatimatu Zahra a.s. wannan wani taklifi ne wanda ya hau akan dukkan al’ummar musulmi a kowane lokaci kuma a ko’ina suke, saboda haka bai kebanta da wasu mutane ba sabanin wasunsu

  Soyayya ga Zahra a.s. tana matsayin girmama manzon Allah ne s.a.a.w. haka tunawa da musibar da ta auku akan sayyida Zahra a.s.

 Saboda haka babu wani lokaci da zamu iya mantawa da wanann musiba, sannan tarihi yana mai  sheda akan irin zalunci da aka yi wannan baiwar Allah Zahra a.s. Imam amirul Muminin Ali a.s. bayan wafatin Zahra ga abin da yake cewa: “Bakin ciki da nake acikinsa wani abu na har abada wanda  ba zai wuce ba”. Shin tare da wannan Magana ta Imam a.s. shi’ar Ali a.s. suna iya kasancewa ba tare da wanann bakin ciki ba?

  Bisa wanann ne ya wajaba kan shi’a ranar laraba uku ga watan Jumada thani wanda ya yi daidai da ruwaya ingantacciya cewa ita ce ranar shahadar sayyida Zahra a.s. su fito kwansu da kwarkwata domin nuna juyayinsu da wannan rana, acikin godiyar Allah jamhuriyar musulunci ta sanar da wannan rana a matsayin hutu domin masoya Zahra a.s. su samu damar nuna juyajyinsu akan wannan rana.

Muhammad Fadhil lankarani
29-4-1383

5
Da sunan Allah mairahma maijinkai

Amincin Allah ya tabbata ga siddikatu shahida Azzahra a.s.

Mun kasance acikin kwanakin shahadar sayyida Zahra a.s. Fatimatu zahra a.s. wadda take masoyiyar manzon tsira Muhammad s.a.a.w. sannan matar Shugaban muminai Ali a.s. kuma mahaifiyar Aimma goma sha daya a.s.

Sayyida Zahra a.s. ita ce shugaban dukkan matan duniya. Duk da cewa acikin kur’ani Allah madaukaki dangane da Maryam a.s. yana cewa:”Na zabe ki akan matan duniya” amma kamar yadda ya zo a ruwa abin nufi shi ne Allah ya zabeta acikin matan duniya ta yadda ta haifi Isa a.s. ba tare da miji ba. Wannan al’amari ya kebanci sayyida  Maryam a.s. Amma damgane da girma da daukakar Zahra a.s. ta fuskar ilimi da tsarki da isma da bautar Allah ta daukaka akan dukkan matan duniya .

  Saboda haka ya wajaba ga al’ummar musulmi ranar uku ga watan Jumada thani  wanda ya dace da ranar shahadar sayyida Zahra a.s. su gudanar da taruka domin nuna juyayi da wannan ranar, domin nuna muhimmanci wannan rana jamhuriyar musulunci ta bayar da hutu domin al’ummar musulmi su samu damar gudanar da wannan taruka na makokin shahada Siddika zahra a.s. don haka wannan ranar Ashura ce ta biyu. Saboda haka kamar yadda ya kasance a shekarun baya ta yadda wannan al’umma masoya Zahra a.a.s suka aiwatar da nauyin da ya hau kansu na girmama wannan rana, anan ya kamata in mika godiyata ta musamman ga al’ummar musulmi. Babu shakka a fili yake girmama duk wani abu da ya shafi sayyida Zahra a.s. girmama manzon ne s.a.a.w. sannan yana matsayin ladar manzancin manzo s.a.a.w.

 Al’ummar Iran mai girma ta hanyar riko da igiyar ahlul bait a.s. kuka iya samar da daular musulunci a Iran kuma da wanann ne hukumar musulunci ta Iran take samun karfin tafiya. Saboda haka ya zama tilas mu fahimci cewa sirrin nasararmu shi ne riko da hanyar ahlul bait a.s. da kuma kai kukanmu zuwa ga ruhunan wadanan bayin Allah ahlul bait a.s. saboda haka zatinmu shi ne shi’anci da musulunci na gaskiya. Da fatar Allah madaukaki ya sanya mu karakashin inwar zahra a.s.

Muhammad Fadhil Lankarani
15-4-1384